Go Again Dujiman Katsina Movement

Go Again Dujiman Katsina Movement

Share

An bude wannan Shafi ne domin Kawo irin cigaban da Dujiman katsina Abdullahi Aliyu Ahmed yake kawowa

26/07/2026

Go Again Dujiman Katsina 2027

14/07/2026

Duk a cikin Shirye-shiryen Nasarar Dujiman Katsina 2027

Details coming

Photos from Go Again Dujiman Katsina Movement's post 02/07/2026

DUJIMA MATAKI NA GABA

An sake buɗe sabon babi a tafiyar siyasar ƙananan hukumomin Musawa da Matazu bayan da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) ta tabbatar da Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina) a matsayin ɗan takarar Jam'iyyar APC na kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Musawa da Matazu.

An gudanar da taron ranar Laraba, 1 ga Yuli, 2027, a Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya miƙa wa Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina) takardar shaidar tabbatar da takararsa, a gaban manyan shugabanni da jiga-jigan Jam'iyyar APC.

Bikin ya samu halartar Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar Katsina, Dr. Bashir Gambo Saulawa, NLA Barr. Murtala Aminu Kankia, tare da sauran manyan masu ruwa da tsaki na jam'iyyar, waɗanda s**a bayyana wannan mataki a matsayin wani gagarumin ci gaba ga tafiyar jam'iyyar a yankin Musawa da Matazu.

Tabbatar da Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina) na zuwa ne a daidai lokacin da magoya bayan jam'iyyar ke ci gaba da bayyana kwarin gwiwarsu kan cewa zai kawo wakilci mai inganci da kusanci da al'umma, tare da ba da fifiko ga ci gaban matasa, mata da kuma bunƙasa ayyukan raya ƙasa a mazabun.

30/06/2026

DAGA OFISHIN DAN MAJALISAR TARAYYA NA MUSAWA DA MATAZU.

Ana sanar da matasan Musawa da Matazu, musamman waɗanda s**a nemi aikin CDCFIB, cewa a yau ma an ƙara fitar da sunayen wasu daga cikin waɗanda aka yiwa shortlisting.

Saboda haka, ku cigaba da duba portal ɗinku. Ga waɗanda basu ga sunayensu ba, su kwantar da hankalinsu, domin ana cigaba da fitar da sunaye a matakai daban-daban.

Allah Ya ba kowa sa'a.

Signed;
Affan Sani Matazu
Legislative Aide
Musawa/Matazu
Federal constituency.

26/06/2026

SAƘON JAJE DA TA'AZIYYA

A madadin Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Mazabar Musawa da Matazu, Hon. Abdullahi Aliyu Ahmed Dujiman katsina
muna miƙa saƙon ta'aziyya mai cike da alhini ga iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu, a garin Sayaya, Ƙaramar Hukumar Matazu, da kuma ɗaukacin al'ummar Jihar Katsina, bisa mummunan harin da ya yi sanadin rasa rayukan mutane bakwai (7)

Wannan lamari abin takaici ne ƙwarai, kuma ya girgiza zukatanmu. Mun yi Allah wadai da wannan danyen aiki na rashin tausayi da ya salwantar da rayukan bayin Allah. Rayuwar ɗan Adam tana da tsarki, kuma babu wani dalili da zai halasta zubar da jinin wadannan bayin Alllah

Muna addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa waɗanda s**a rasu, Ya sanya su cikin Aljannatul Firdausi, Ya bai wa iyalansu da al'ummar Sayaya haƙurin jure wannan babban rashi.

Haka kuma muna roƙon Allah Ya ba waɗanda s**a jikkata cikakkiyar lafiya cikin gaggawa.

Muna kira ga jami'an tsaro da hukumomin da abin ya shafa da su ɗauki matakan gaggawa wajen kamo masu hannu a wannan ta'asa tare da tabbatar da cewa an hukunta su bisa tanadin doka, domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma da hana sake aukuwar irin wannan mummunan lamari.
Muna tabbatar wa al'ummar Musawa da Matazu cewa za mu ci gaba da mara wa duk wani ƙoƙarin samar da zaman lafiya da tsaro baya, domin al'ummarmu ta rayu cikin kwanciyar hankali.

Allah Ya jiƙan mamatan, Ya gafarta musu, Ya ba iyalansu haƙuri da juriya, Ya kare ƙasarmu daga sharrin miyagu, Ya tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a Matazu, Musawa, Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya. Amin Ya Rabbal Alamin.

A Madadin Dan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Mazabar Musawa da Matazu

04/06/2026

Kungiyar GO AGAIN DUJIMA KATSINA MOVEMENT na godiya Leader Alh. Yusuf Ali Musawa

Photos from Go Again Dujiman Katsina Movement's post 01/06/2026

HON. ABDULLAHI ALIYU AHMAD DUJIMAN KATSINA YA RABA GORON SALLAH NA RIYAL 35,100 GA MAHAJJATAN KATSINA A KASAR SAUDIYYA

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Musawa/Matazu, Hon. Abdullahi Aliyu Ahmad Dujiman Katsina, ya bada tallafin goron Sallah na Riyal 35,100 kwatankwacin Naira 12,987,000 ga mahajjatan jihar Katsina da s**a fito daga gundumar Musawa da Matazu a kasar Saudiyya.

Wadanda s**a amfana da tallafin sun hada da mahajjatan Musawa/Matazu, mambobin Gwagware Foundation, malamai masu wa’azi na jihar (State Preachers), Loaders na Alhazai, mambobin Hukumar Alhazai (Board Members) da sauran al’ummar jihar Katsina da ke kasa mai tsarki domin gudanar da aikin Hajji.

A rabon tallafin, mahajjatan da s**a fito daga kananan hukumomin Musawa da Matazu sun samu Riyal 300 kowannensu, yayin da sauran wadanda s**a amfana s**a samu Riyal 200 kowanne.

Hon. Dujiman Katsina ya bayyana cewa tallafin na daga cikin kokarinsa na tallafawa al’umma musamman a wannan lokaci na ibada da neman kusanci ga Allah Madaukakin Sarki.

Hakazalika, ya yi kira ga mahajjatan da su kara yawaita addu’o’in zaman lafiya, tsaro da ci gaban jihar Katsina baki daya, musamman yankunan Musawa da Matazu, tare da addu’ar Allah Ya kawo karshen matsalolin rashin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar.

Ya kuma roki mahajjatan da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’ar samun nasara da dacewa wajen gudanar da ayyukan al’umma cikin gaskiya da adalci.

Wadanda s**a amfana da tallafin sun bayyana jin dadinsu tare da mika godiya ga Hon. Abdullahi Aliyu Ahmad Dujiman Katsina bisa wannan kyauta da ya ba su, inda s**a ce tallafin ya zo a daidai lokacin da ake matukar bukatarsa, musamman a wannan lokaci na gudanar da ibadun aikin Hajji.

Allah Ya karbi ibadun mahajjata baki daya tare da dawo da su gida lafiya. Ameen.

26/05/2026

Arafah Mubarak

Want your business to be the top-listed Beauty Salon in Katsina?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Address

Musawa Local Government
Katsina